‘Karya ne – gwamnatinmu ba ta wani yaki da rashawa’

Muhammadu Buhari

Wata fitacciyar ‘yar siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC mai mulki, Hajiya Naja’atu Mohammed ta ce babu gaskiya cikin yaki da gwamnatinsu ke yi da cin hanci da rashawa.

Hajiya Naja’atu Muhammad na cikin wadanda suka rika tallata Muhammadu Buhari a matsayin mafi cancanta da zama shugaban kasa a zaben 2015.

‘yar siyasar ta yi wannan jawabi ne dangane da jerin bidiyon da aka wallafa da ke zargin gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje na karbar kudaden da aka ce cin hanci ne daga hannun ‘yan kwangila.

‘Ihun da aka yi wa Buhari abun kunya ne’

Buhari ya sha tafi da ihu a Majalisa

Ta kalubalanci gwamnatin tasu a kan rashin gudanar da bincike kan lamarin, duk da ikirarin da jami’anta ke yi da cewa suna yaki da rashawa.

“Idan zargi ne, me ya sa ba a yi bincike ba? Ai, idan ba a yi zargi ba, ba za a yi bincike ba. Idan ba a yi bincike ba, ai ba za a gano gaskiya ba.”

Ta ce a iyakar saninta, kotu ba ta isa ta hana ‘yan sanda ko Hukumar EFCC gudanar da bincike ba.

More from this stream

Recomended