Karin Mutum 404 Sun Kamu Da COVID-19 a Najeriya

Adadin wadanda suka kamu da cutar COVID-19 a Najeriya ya zarta 42,000 a ranar Laraba 29 ga watan Yuli, a cewar hukumar da ke sa ido kan cututtuka masu yaduwa wato NCDC, yayin da cutar ke ci gaba da yaduwa a kasar da ta fi mai yawan al’umma a nahiyar Afrika.

A bayannan da ta ke fidda wa a kowacce rana a shafinta na Twitter, hukumar NCDC ta ce an samu karin mutum 404 da suka kamu da cutar abinda ya sa gaba dayan adadin ya kai 42,208.

A cewar hukumar, cikin mutum 42,208 da suka kamu da cutar ya zuwa yanzu, 19,004 sun warke kuma an sallame su daga asibiti yayin da mutum 873 suka mutu.

Hukumar ta kuma ce an samu karin adadin ne daga jihohi 19 na kasar: Lagos-106, Birnin tarayya Abuja-54, Rivers-48, Plateau-40, Edo-29, Enugu-21, Oyo-20, Kano-18, Ondo-15, Ogun-10, Ebonyi-9, Ekiti-8, Kaduna-6, Cross River-5, Kwara-4, Anambra-3, Delta-3, Imo-2, Nasarawa-2, sai kuma Borno-1.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...