Karin mutane 10 sun kamu da cutar Coronavirus a Najeriya – AREWA News

An sake samun karin sabbin mutane 10 da suka kamu da cutar Covid-19 a Najeriya ciki harda birnin tarayya Abuja.

Ministan lafiya,Osagie Ehanire shi ne ya sanar da haka ranar Asabar.

Ya ce an samu wadanda suka kamu da cutar a birnin tarayya Abuja da kuma jihohin, Ekiti,Ogun,Lagos.

Hakan na nufin cewa an samu jumullar mutane 22 da suka kamu da cutar a Najeriya.

Dukkanin mutane ukun biyu maza da kuma mace daya da aka samu suna dauke da cutar a Abuja sun dawo ne daga kasashen waje tsakanin ranakun 14 zuwa 18 ga wata.

More from this stream

Recomended