Kar a yi saurin yanke wa gwamnatin Tinubu hukunci—in ji Yakubu Gowon

Tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon, ya yi gargadin cewa kada a yi gaggawar yanke hukunci kan ayyukan gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Gowon ya bayyana haka ne ga manema labarai a fadar shugaban kasa jiya bayan ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa.

Tsohon shugaban kasar ya ce ya shawarci Tinubu da kada ya damu da sukar da ake yi wa gwamnatinsa a halin yanzu.

Dattijon ya ce ya yi wuri a yanke hukunci a kan gwamnatin Tinubu.

Ya ce “To, ina gaya masa cewa babu wani shugaban Najeriya da zai iya kawo wannan matakin kuma bai samu dukkan rahotannin abin da ake fada a kansa ba.”

“Ina ganin gwamnati na iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance matsalolin kasar nan daban-daban.”

Wannnan zuwa ne a daidai lokacin da rayuwa ta yi ƙunci wa ƴan Najeriya yayin da farashin kayayyaki ke ci gaba da yin tashin gwauron zabi.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...