Kanar DC Bako: ‘Yan Najeriya sun fusata kan kisan da Boko Haram ta yi wa Kwamandan sojin ƙasar

Kanar DC Bako

Bayanan hoto,
Kanar DC Bako yana cikin sojojin da suka jagoranci yaki da Boko Haram

Kisan da ake zargi mayakan kungiyar Boko Haram sun yi wa wani Kwamandan rundunar sojin Najeriya ya yi matukar fusata wasu ‘yan kasar musamman wadanda ke amfani da shafin Twitter.

A ranar Litinin ne rundunar sojin kasar ta bakin rundunar Lafiya Dole ta tabbatar da mutuwar Kanar DC Bako, wanda ta ce ya mutu sakamakon raunuka da ya samu bayan kwanton-baunan da mayakan Boko Haram suka yi wa tagawarsa a yankin Sabon Gari-Wajiroko kusa da Damboa jihar Borno ranar Lahadi.

Dakarun da yake jagoranta sun ragargaji mayakan da suka yi musu kwanton-bauna inda suka kashe ‘yan ta’adda da dama sannan suka kwato makamai da na’urori, a cewar sanarwar da mai magana da Runduna Ta Bakwai Ado Isa ya fitar.

“Abin bakin ciki shi ne an raunata shi a lokacin da yake ba-ta-kashi kuma nan take sojin sama na rundunar Lafiya Dole suka dauke shi zuwa asibitin Runduna ta Bakwai 7 da ke Maimalari. Marigayi babban jami’in runsunar sojin yana cike da kazar-kazar kuma ya yi sallar Asuba da safiya yau kafin mutuwarsa a asibitin,” a cewarsa.

Wannan labari ya yi matukar bata ran ‘yan Najeriya da ke amfani da Twitter, inda suka rika yin amfani da maudu’i mai taken “Boko Haram” don bayyana fushinsu kan gwamnatin Najeriya da rundunar sojin kasar da ma abin da suka ce yaudararsu da ake yi cewa an murkushe Boko Haram amma “har yanzu sai ci gaba da kashe sojoji da farar hula take yi.”

An kashe Kanar Abu Ali, an kashe Kanar DC Bako

Bayanan hoto,
Masu amfani da Twitter sun ce dole gwamnatin Najeriya ta sauya salo wajen yaki da Boko Haram

A sakon da ya wallafa, Sam Adeyemi, ya ce ana kashe iyaye da ‘yan uwan mutane amma “babu”abin da gwamnatin Buhari take yi sai yin afuwa ga ‘yan Boko Haram take yi.

Kauce wa Twitter, 1

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 1

“An kashe Kanar Bako, wa za a kashe nan gaba? Ya kamata Buratai ya gaya mana shirinsa. Bai kamata ya bari a kashe mutanenmu baki daya ba kafin ya sauka daga mukamin Hafsan sojin Najeriya,” a cewarsa.

Ita ma Mohnice ta ce: “Ya kamata shugaban kasar ya cire Hafsoshin tsaro daga kan mukamansu ba tare da bata lokaci ba. Ya kamata a saurari korafin ‘yan Najeriya kan wadannan kashe-kashe marasa kan gado da Boko Haram ke yi wa sojojinmu”.

Kauce wa Twitter, 2

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 2

Shi kuwa Comrade Mazi Okay yaba wa Kanar DC Bako ya yi, sannan ya ce kisansa wani babban koma-baya ne a yaki da Boko Haram.

Kauce wa Twitter, 3

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 3

“Babbar katanga ta rushe, kuma hakan babban koma-baya ne ga yakin da Najeriya take yi da Boko Haram. Kafin mutuwarsa a safiyar nan, Kanar Bako mutum ne da babu kamarsa a yaki da Boko Haram. Mutumin da ya murkushe sanna ya lalata maboyar Boko Haram a jihar Yobe,” in ji shi.

A nasa bangare, AS Auwal ya yi waiwaye kan kisan da mayakan Boko Haram suka yi wa Kanar Abu Ali, yana mai cewa yanzu sun sake kashe wani jajirtaccen sojin na Najeriya.

Kauce wa Twitter, 4

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 4

More from this stream

Recomended