Gwamnatin Amurka ta dakatar da tallafin kusan dala miliyan 200 da take bawa ƙasar Nijar.
Dakatar da tallafin ya yi dai-dai da sashe na 7008 kasafin kuÉ—in shekara na ma’aikatar harkokin wajen Amurka.
Hakan na zuwa ne biyo bayan jerin takunkumi iri-iri da aka ƙaƙabawa kasar tun bayan da sojoji suka hamɓarar da gwamnatin shugaban kasa, Mohamed Bazoum.
A wata sanarwa ranar Talata, Matthew Miller mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ya tabbatarwa da Æ´an kasar ta Nijer cewa za su cigaba da amfana da tallafin ayyukan jin kai daga Amurka da ya shafi abinci da kuma sashen kiwon lafiya.
Amurka ta kuma nanata kiranta na sakin tsohon shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum tare da iyalinsa da kuma dukkan mutanen da ake tsare da su.