Juyin mulki:Amurka ta dakatar da tallafin dala miliyan $200 da take bawa Niger

Gwamnatin Amurka ta dakatar da tallafin kusan dala miliyan 200 da take bawa ƙasar Nijar.

Dakatar da tallafin ya yi dai-dai da sashe na 7008 kasafin kuÉ—in shekara na ma’aikatar harkokin wajen Amurka.

Hakan na zuwa ne biyo bayan jerin takunkumi iri-iri da aka ƙaƙabawa kasar tun bayan da sojoji suka hamɓarar da gwamnatin shugaban kasa, Mohamed Bazoum.

A wata sanarwa ranar Talata, Matthew Miller mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ya tabbatarwa da Æ´an kasar ta Nijer cewa za su cigaba da amfana da tallafin ayyukan jin kai daga Amurka da ya shafi abinci da kuma sashen kiwon lafiya.

Amurka ta kuma nanata kiranta na sakin tsohon shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum tare da iyalinsa da kuma dukkan mutanen da ake tsare da su.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...