Juyin mulki:Amurka ta dakatar da tallafin dala miliyan $200 da take bawa Niger

Gwamnatin Amurka ta dakatar da tallafin kusan dala miliyan 200 da take bawa ƙasar Nijar.

Dakatar da tallafin ya yi dai-dai da sashe na 7008 kasafin kuɗin shekara na ma’aikatar harkokin wajen Amurka.

Hakan na zuwa ne biyo bayan jerin takunkumi iri-iri da aka ƙaƙabawa kasar tun bayan da sojoji suka hamɓarar da gwamnatin shugaban kasa, Mohamed Bazoum.

A wata sanarwa ranar Talata, Matthew Miller mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ya tabbatarwa da ƴan kasar ta Nijer cewa za su cigaba da amfana da tallafin ayyukan jin kai daga Amurka da ya shafi abinci da kuma sashen kiwon lafiya.

Amurka ta kuma nanata kiranta na sakin tsohon shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum tare da iyalinsa da kuma dukkan mutanen da ake tsare da su.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]