Rahotanni sun ce wani jirgin ruwan yakin Iran ya nutse a tekun Sri Lanka bayan wani hari da aka kai masa.
Rahoton ya ce sojojin ruwa da na sama na Sri Lanka sun gudanar da aikin ceto, inda suka kubutar da sama da Iraniyawa 30 da ke cikin jirgin samfurin “IRIS Dena.” Ana ci gaba da neman sama da mutum 100 da har yanzu ba a san inda suke ba.
Sai dai gwamnatin Sri Lanka ta musanta rahotannin da ke cewa an kai wa jirgin hari, amma ta tabbatar cewa jami’an tsaronta na gudanar da aikin ceto a yankin.
A wani bangare kuma, rahotanni sun nuna cewa tankokin mai da dama sun makale a mashigar Hormuz bayan Iran ta hana zirga-zirga a yankin.
Bayanan da ke shigowa sun nuna cewa kusan tankokin mai 200 ne suka kasa motsi a mashigar Hormuz, inda wasu daga cikinsu ke tunanin ko za su juya su koma inda suka fito.
Jirgin Yakin Iran Ya Nutse A Tekun Sri Lanka, An Ceto Mutane Sama Da 30

