Akalla shanu 50 ne a jiya jirgin kasa dake kan hanyarsa ta zuwa Abuja ya markade su har lahira, Kwamishinan ƴansandan jihar Kaduna, Ahmad Abdulrahman shine ya bayyana haka jiya.
Ya ce rundunar ta samu kiran kai daukin gaggawa akan hatsarin da misalin 11:45 na safe inda ya kara da cewa shi da kansa ya jagoranci manyan jami’an rundunar ya zuwa wurin da abin yafaru dake Kasarami a gundumar Jere karamar hukumar Kagarko ta jihar Kaduna.
“Lokacin da muka isa wurin mun gano cewa ba kamar yadda rahotannin farko ke cewa harin yan ta’adda ne, gaskiyar abinda yafaru hatsari ne,”kwamishinan ya ce.
A cewarsa wasu fulani da suka kwana a Kasarami sun tambaya ko za su iya tsallakawa da shanunsu amma aka ba su gurguwar shawara cewa jirgi baya wucewa ranar Lahadi.
” A daidai lokacin da suke tsallakawa ne takan digar jirgin sai jirgi mai gudu daga tashar Rigasa akan hanyarsa ta zuwa Abuja ya nufi wurin da suke tsallakawa ya kuma markade shanu 52 har lahira.”
Ya ce an bayar da umarnin yanka shanu 27 da suke da rai inda aka sayar da su domin rage asara.
Fulanin na kan hanyarsu ne ta zuwa jihar Katsina.