Jirgin ƙasar Abuja zuwa Kaduna ya kauce daga kan digarsa a Abuja

Fasinjoji da dama ne suka yi carkwo-carkwo bayan da jirgin ƙasa da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna ya sauka daga kan digarsa a tashar Asha dake birnin tarayya Abuja.

Ɗaya daga cikin fasinjojin dake cikin jirgin ya faɗawa jaridar The Cable cewa jirgin ya kauce daga kan digarsa ne da misalin ƙarfe 03:30 na rana ƙasa da mintuna 30 bayan da ya bar tashar Kubwa.

“Fasinjoji sun yi carkwo-carkwo suna zaman jira kuma babu alamun zuwan hukumomi da aka sanarwa da faruwar lamarin,”

Wannan ne karon na biyu cikin makonni biyu da jirgin ƙasar ya ke sauka daga kan layinsa.

A ranar 26 ga watan Mayu jirgin ya kauce daga kan layinsa  bayan da ya baro tashar Rigasa dake Kaduna akan hanyarsa ta zuwa Abuja.

Tarago uku ne ya sauka daga kan digar jirgin amma babu  mutanen da suka jikkata.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...