Jihohi 7 sun kwashe ɗalibansu daga jami’ar Jos

Aƙalla gwamnatocin jihohi  7 ne suka kwashe ɗaliban su kusan 1630 daga jami’ar Jos biyo bayan tashin hankalin da aka samu a jihar Filato.

A ranar 27 ga watan Maris ne wasu yan bindiga su ka kai farmaki Unguwar Rukuba inda su ka kashe aƙalla mutane 28 tare da jikkata wasu da dama.

Gwamnatin jihar ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 48 biyo bayan harzuƙa da mutane da su ka yi a kafafen soshiyal midiya.

Saboda kusancin jami’ar da inda rikicin ya faru ya sa mahukuntar jami’ar Jos su ka dakatar da jarabawar da ake yi a makon tare da sauya lokacin yin jarabawar ya zuwa bayan hutun bukukuwan Ista.

A ranar ne gwamnatin jihar Delta ta sanar da kwashe ɗalibai yan asalin jihar su 34 saboda yanayin tsaro.

Itama jihar Lagos ta sanar da kwashe ɗalibai yan asalin jihar su 230 kamar yadda jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jihar, Mamud Hassan ya bayyana.

Jihar Adamawa ta kwashe ɗalibanta su 120, sai jihar Bauchi da ta kwashe sai jihar Bauchi da ta kwashe ɗalibai 60.

Sauran jihohi da suka kwashe ɗalibansu sun haɗa da jihar Cross River da ta kwashe ɗalibai 37 da kuma jihar Benue da ta kwashe ɗalibai 600 ita ma jihar Nasarawa ta kwashe ɗalibai 545.

More from this stream

Recomended