Jihar Neja za ta riƙa biyan  ₦80,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago ya amince a riƙa biyan ₦80,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan jihar.

Gwamnan ya amince da fara biyan kuɗin a matsayin mafi ƙarancin albashi a ranar Juma’a  a yayin wani taron ganawa da wakilan ƙungiyar kwadago ta jihar a Minna babban birnin jihar.

A wani saƙo da ya wallafa a shafin X, Bago ya ce jihar ta Neja ta amince ta fara biyan mafi ƙarancin albashi.

A ƴan kwanakin nan dai ana ta cigaba da samun ƙarin jihohi da suke tabbatar da fara biyan mafi ƙarancin albashin da gwamnatin tarayya da kuma ƙungiyar ƙwadago suka amince da shi.

More News

Jam’iyar NNPP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano

Jam'iyar New Nigeria People Party NNPP ta lashe zaɓen  dukkanin kujerun ƙananan hukumomin jihar Kano 44. Farfesa Sani Malumfashi shugaban hukumar zabe mai zaman kanta...

Jam’iyar NNPP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano

Jam'iyar New Nigeria People Party NNPP ta lashe zaɓen  dukkanin kujerun ƙananan hukumomin jihar Kano 44. Farfesa Sani Malumfashi shugaban hukumar zabe mai zaman kanta...

Wani sojan ruwan Najeriya ya hallaka abokin aikinsa a Zamfara

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kama wani sojan ruwa mai suna A. Akila bisa zarginsa da kashe abokin aikinsa.An tura Akila zuwa sansanin Forward Operating...

Tinubu da Atiku sun haɗu a Masallacin Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu  sun haɗu da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar a babban masallacin ƙasa dake Abuja. Mutanen biyu sun haɗu ne...