Japan Ta Fara Fitar Da Man Ajiya Don Rage Tasirin Rikicin Iran

Japan ta fara fitar da wani ɓangare na man da ta adana domin rage fargabar ƙarancin mai da ake dangantawa da rikicin da ya shafi Iran.

Rahotanni sun nuna cewa ƙasar ta ɗauki wannan mataki ne bisa raɗin kanta, tun kafin a fara aiwatar da shirin haɗin gwiwa na ƙasashen da ke cikin Hukumar Makamashi ta Duniya (IEA) na sakin man ajiya.

Japan na cikin ƙasashen da ke dogaro sosai da shigo da mai daga yankin Gabas ta Tsakiya. Hakan ya sa ta tara ɗimbin man ajiya, wanda ake ganin yana daga cikin mafi yawa a duniya.

An fara wannan tsarin tanadin man ne tun bayan matsanancin ƙarancin mai da duniya ta fuskanta a shekarun 1970, wanda ya samo asali daga rikicin siyasa a yankin Gabas ta Tsakiya.

More from this stream

Recomended