Jam’iyyar PDP A Bauchi Ta Bukaci Bala Mohammed Ya Ci Gaba Da Zama A Jam’iyyar

Jam’iyyar PDP a jihar Bauchi ta bukaci gwamnan jihar, Bala Mohammed, da ya ci gaba da kasancewa a jam’iyyar duk da rade-radin da ake yi kan yiwuwar ficewarsa.

Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar a jihar, Mannasseh Marti, wanda ke da alaƙa da ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa babu wata matsala mai tsanani a cikin jam’iyyar, yana mai cewa PDP na nan daram kuma tana da ƙarfi.

Ya ce jam’iyyar ta samu karɓuwa daga al’umma tun daga shekarar 2019, tare da aiwatar da ayyukan da suka inganta rayuwar jama’a a jihar.

More from this stream

Recomended