Jam’iyun siyasa 56 sun shirya fafatawa zaben 2019-INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa INEC ta ce jam’iyun siyasa 56 cikin 91 da aka yiwa rijista a kasarnan sun shirya shiga zaben shekarar 2019.

Obo Effanga, kwamishinan zaben jihar Rivers shine ya bayyana haka ranar Juma’a lokacin da yake ganawa da yan jaridu a Fatakwal.

Ya ce INEC na sha’awar shigar dukkanin jam’iyyun 91 inda ya kara da cewa hukumar za ta yi hulda ne kawai da jam’iyun siyasar da suka yi rijistar shiga zaben.

Kwamishinan zaben ya tabbatarwa da mutanen jihar Rivers cewa hukumar ta shirya gudanar da zabe mai cike da gaskiya da adalci ya kara da cewa za a tabbatar an tanadi dukkanin kayayyakin da ake bukata gabanin ranar zaben.

Effanga ya ce duk wani mai kada kuri’a da ba a tantance da na’urar Card Reader ba to ba zai samu damar kada kuri’a ba.

More News

DA ÆŠUMI-ÆŠUMI: DSS sun cafke Sowore a filin jirgin na Legas

Jami'an Hukumar Ƴansandan Farin-kaya ta DSS sun kama Omoyele Sowore, jagoran kungiyar  #RevolutionNow Movement da ke adawa da gwamnati a filin jirgin sama na...

Ƴan bindiga sun Æ™one ginin hedkwatar Æ™aramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu Æ´anta’adda da ke da alaÆ™a da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa Æ´an’adda a Borno, wani kwamanda ya miÆ™a wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...