
Babbar kotun tarayya dake Ibadan babban birnin jihar Oyo ta soke babban taron jam’iyyar PDP da aka yi ranar 15 ga watan Nuwamba a jihar inda aka zaɓi sababbin shugabannin jam’iyar.
A hukuncin da kotun ta yanke ranar Juma’a, Uche Agomoh alkalin kotun ya hana shugabannin jam’iyar da aka zaba wurin taron ayyana kansu a matsayin shugabannin jam’iyar
Agomoh ya bayyana cewa babban taron zaben shugabannin jam’iyar da aka gudanar a cikin watan Nuwamba ya saba umarnin da kotun ta bayar na kada a gudanar da shi.
Alkalin ya zartar cewa za a iya jagorantar jam’iyar PDP ne kaɗai ta hanyar shugabancin kwamitin riko har ya zuwa lokacin da za a gudanar da wani babban taron na zaɓen shugabanni.
Tsagin jam’iyar PDP karkashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki wanda aka zaba a wurin taron su ne su ka shigar da kara gaban kotun inda suka nemi ta ayyana su a matsayin a matsayin halastattun shugab

