Mohammad Muhammad, jami’in ‘yan sanda a rundunar jihar Borno, ya mayar da Naira miliyan 2.6 da aka tura masa ba da niyya ba a asusunsa na banki.
Nahum Daso, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, ya yabawa jami’in bisa gaskiya da rikon amana, yayin da yake shiyarin ɗin wani sako da Bello Jafar ya wallafa a Facebook.
A cikin sakon, Daso ya ce: “Ina so in bayyana godiyata ga Mohammad Alhaji Muhammad, kwastoma mai aminci na UBA kuma jami’in ‘yan sanda mai cikakken rikon amana.”
Jafar ya kara da cewa matakin da jami’in ya dauka yana nuna gaskiya, nagarta, da kwarewar tarbiyya. Ya ce: “Halayensa ya dace da dabi’un da ake sa ran jami’in ‘yan sanda ya mallaka, kuma abin koyi ne da ya kamata a yaba masa.”
Ya kara da cewa: “Ayyuka irin wannan na kara amincewar jama’a da nuna muhimmancin rikon amana a rayuwa ta aiki da ta kashin kai.”
Jami’in ‘Yan Sanda Ya Mayar da N2.6m Da Aka Tura Masa Bisa Kuskure

