Rahotanni daga jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya sun nuna cewa jami’an tsaro sun yi nasarar hallaka wasu manyan ’yanbindiga kimanin 65 a wani samame.
Bayanan sun ce daga cikin waɗanda aka kashe har da ’ya’yan fitaccen jagoran ’yanbindiga, Ado Aleiro guda uku, waɗanda suka dade suna addabar yankin Tsafe.
Wani ɗan jarida mai bincike kan ayyukan ’yanbindiga a yankin, Mannir Sani Fura Girke, ya shaida wa manema labarai cewa lamarin ya faru ne lokacin da ’yanbindigar ƙarƙashin jagorancin Ado Aleiro suka yi yunƙurin kai hari kan sabon sansanin jami’an tsaro da aka kafa a garin Ƙuncin Kalgo, inda jami’an tsaron suka mayar da martani.
“Tun maraicen ranar Asabar ɓangarorin biyu suke musayar wuta tsakaninsu har zuwa wayewar garin Lahadi ake fafatawa”, in ji shi.
Ya ƙara da cewa artabun ya yi sanadin mutuwar kusan ’yanbindiga 65, ciki har da ’ya’yan Ado Aleiro.
“Daga ciki akwai ’ya’yan Ado Aliero na cikinsa har guda uku, ciki har da babban ɗansa, Sarki da Ahmadu da Iliya, duka ’ya’yansa ne na cikinsa, kuma an kashe su”, in ji ɗan jaridar.
Haka kuma, ya ce an kashe wasu manyan kwamandojin tawagar ’yanbindigar, ciki har da Kacalla Hukuma da Kacalla Dogo Burti da Kacalla Baƙin Sifindi da Kacalla Mani Mugu da Kacalla Iliya mai Rasha.
“Duka waɗannan su ne manyan jagororin tawagar da suka jagoranci wannan faɗan”, kamar yadda ya bayyana.
Mannir Girke ya kuma ce sabon sansanin sojin da aka buɗe a Ƙuncin Kalgo na da matuƙar muhimmanci, domin yankin na kusa da dajin Munhaye da aka dade ana danganta shi da mafakar ’yanbindiga.
Ya ƙara da cewa wannan wuri hanya ce da ’yanbindiga ke bi wajen kai hare-hare zuwa sassan Tsafe, Gusau, Faskari, Bakori da Kankara, yana mai cewa kafa sansanin a wurin babbar nasara ce ga rundunar tsaro.
Jami’an Tsaro Sun Kashe Manyan ’Yanbindiga 65 A Zamfara

