Jami’an tsaro sun kama mai garkuwa da mutane a Borno

Dakarun soja na rundunar tsaro ta  29 Task Force Brigade tare da haɗin gwiwar dakarun kungiyar Civilian JTF sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne a kasuwar Benisheikh dake karamar hukumar Kaga ta jihar Borno

Wasu majiyoyi jami’an tsaro sun bayyana cewa wanda ake zargin mai suna Charu Madu an kama shi ne a ranar 30 ga watan Maris da misalin karfe 05:45 na yamma biyo baya samun sahihan bayanan sirri daga wasu mutane.

A cewar majiyar bayan samun nasarar kama shi an gano bindiga kirar AK-47 guda a tare da shi tare da harsashi da kuma kuɗi naira 4500.

Kawo yanzu ana tsare da wanda ake zargi inda ake cigaba da gudanar da bincike.

More from this stream

Recomended