Hadin gwiwar jami’an tsaron Najeriya sun kaddamar da farautar wasu mutane da ƴanbindiga suka sace a garin Kurfa da ke karamar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.
A ranar Juma’a, dan majalisar wakilai na tarayya mai wakiltar yankin ya shaida wa BBC cewa wasu mahara sun kai hari garin, inda suka yi awon gaba da fiye da mutum 150.
Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, DSP Yazid Abubakar ya fitar, ya bayyana cewa maharan sun shiga kauyen ne a kan babura, suna harbin kan mai uwa da wabi, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin firgici.
Sanarwar ta ce jami’an tsaro da suka hada da ƴansanda, sojoji da sauran hukumomin tsaro na ci gaba da kokarin cafke maharan tare da kubutar da mutanen da aka sace.
Kakakin ƴansandan ya kuma ce jami’an tsaron sun gano wasu daga cikin mutanen da suka tsere daga hannun maharan, inda ake kula da lafiyarsu a asibiti.
DSP Yazid Abubakar ya kara da cewa har yanzu ba a tantance ainihin adadin mutanen da aka sace ba, yayin da ake ci gaba da daukar matakan dawo da zaman lafiya a yankin.
Jami’an Tsaro Sun Fara Farautar Masu Garkuwa Da Mutane A Zamfara

