Abdullahi Wase, jakadan Najeriya a kasar Qatar ya rigamu gidan gaskiya.
Tope Elias-Fatile mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasarnan shine ya bayyana mutuwarsa cikin wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce Wase ya yi rashin lafiya na wani dan lokaci kafin rasuwarsa ranar Juma’a da daddare.
“Za a binne marigayin yau a Doha babban birnin kasar da misalin karfe 7:30 na yamma agogon can,”ya ce.
“Ministan harkokin waje, Geoffrey Onyeama ya kadu matuka da samun labarin mutuwarsa inda ya yi addu’ar Allah ya bawa iyalansa da ma kasarnan hakurin jure wannan babban rashin,”
Wase na daya daga cikin jakadun da shugaban kasa Muhammad Buhari ya na da su cikin watan Yulin shekarar 2016, kuma ya fito ne daga jihar Plataeu.