Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito cewa ƙasar ta ƙi amincewa da bukatun da Amurka ta gindaya na kawo ƙarshen yaƙin, inda ta ce za ta dakatar da rikicin ne kawai lokacin da ta ga dama ko aka cika sharuɗan da ta gindaya.
Majiyar tsaro da ba a bayyana sunanta ba ta shaida wa kafar cewa, “Iran za ta kawo ƙarshen yaƙin ne a lokacin da take so, ko kuma aka cika mata sharuɗan da ta gindaya.”
Hukumomi a Iran sun jaddada cewa ba tsagaita wuta suke so ba, yaƙin baki ɗaya ne suke son a dakatar.
Kafar ta kuma ruwaito cewa Iran ta gabatar da sharuɗanta guda biyar:
1. Dakatar da hare-hare da kashe-kashe a ƙasarta.
2. Samar da tsari mai ƙarfi da zai tabbatar ba a sake ƙaddamar da yaƙi a Iran ba.
3. Tabbatar da tsarin biyan diyya.
4. Kawo ƙarshen yaƙi a ƙasar da kuma a hannun sauran ƙungiyoyin da ke da alaƙa da ita a yankin.
5. Ƙasashen duniya su tabbatar da iko da ƴancin Iran wajen gudanar da mashigar Hormuz.
Kafar ta ƙara da cewa Amurka na ƙoƙarin ganin an shiga tattaunawa, amma Iran ta bayyana cewa bukatun Amurka sun yi “tsauri.”
Iran Ta Yi Fatali Da Bukatun Amurka Kan Tsagaita Wuta, Ta Bayyana Sharuɗanta

