Mahukuntan Iran sun tabbatar da mutuwar jagoran addinin kasar, Ali Khamenei, bayan hare-haren da United States da Israel suka kai, kamar yadda kafafen yada labaran gwamnati suka ruwaito.
Tashar talabijin ta kasar ta sanar da faruwar lamarin a ranar Lahadi, tare da ayyana kwanaki 40 na jimami da kuma hutun kasa bakwai domin girmama marigayin wanda ya mulki kasar tun shekarar 1989.
Kungiyar Islamic Revolutionary Guard Corps ta Iran ta yi alkawarin daukar fansa, inda ta yi gargadin cewa za a hukunta wadanda suka aikata harin.
Iran Ta Tabbatar Da Mutuwar Ali Khamenei A Hare-haren Amurka Da Isra’ila, Ta Ayana Jimamin Kwana 40

