Iran Ta Kakkaɓo Jirgin Yaƙi Mara Matuƙi a Shiraz

Rundunar juyin juya halin Iran ta tabbatar da cewa dakarunta sun kwace wani jirgin yaƙi mara matuƙi ƙirar Hermes 900 da aka harba mata.

Rundunar ta bayyana cewa an kwace makamin ne daga sararin samaniyar birnin Shiraz a safiyar yau.

Ana ci gaba da samun tsanantawar yaƙi tsakanin Iran, Amurka da Isra’ila, inda kowanne ɓangare ke kai wa ɗayan hari da makamai masu linzami da jiragen yaƙi mara matuƙi.

More from this stream

Recomended