Iran ta ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami kan wasu sansanonin sojin Amurka da ke Gabas ta Tsakiya, kamar yadda wata sanarwa daga rundunar juyin juya halin Iran ta bayyana a shafin X.
Sanarwar ta ce an harba makamai zuwa sansanin Al Udeid da ke Qatar, da sansanin Arifjan a Kuwait, da kuma sansanin Harir a Iraƙi.
Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Iran, ISNA, ya ruwaito cewa harin mai yawa da aka kai ya kuma nufi rundunar ruwa ta biyar ta Amurka da ke yankin, inda rahotanni suka ce wasu muhimman kayayyakin aikin sojojin Amurka sun lalace.
A wani sako na daban, an bayyana harin a matsayin mafi girma kuma mafi muni da Iran ta kai tun bayan fara wannan rikici.
Sai dai zuwa yanzu jami’an Amurka ba su fitar da wata sanarwa ba kan lamarin.
A lokaci guda kuma an ji kuwwar na’urorin gargadi a sassa da dama na Isra’ila bayan wani sabon harin makamai masu linzami da Iran ta kai, wanda gidan talabijin na Isra’ila ya bayyana a matsayin mafi muni tun fara yakin.
Isra’ila ta ce garkuwar tsaron sararin samaniyarta ta kakkabo makamai da dama da aka harba.
Rundunar juyin juya halin Iran ta ce ta kai harin ne kan wata cibiyar sadarwa ta tauraron dan adam a Haifa da ke arewacin Isra’ila, tare da wasu sansanonin soji.
Haka kuma Iran ta ce ta kai hari kan wasu sansanonin sojin Amurka a yankin, ciki har da wurare a Kurdistan na Iraƙi da Bahrain, yayin da wasu rahotanni suka ambaci hare-hare a Hadaddiyar Daular Larabawa da Saudiyya.
Masana na gargadin cewa matakin Iran na faɗaɗa hare-haren zuwa ƙasashen da ke da alaƙa da Amurka na iya haifar da babbar illa ga tattalin arzikin duniya.
Iran Ta Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Kan Sansanonin Sojin Amurka A Gabas Ta Tsakiya

