Ƙasar Iran ta sanar da fara hare-haren ramuwar gayya bayan hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai mata da safiyar yau.
A wata sanarwa da rundunar sojin Isra’ila ta fitar, wato Israeli Defense Forces, ta ce ta gano makamai masu linzami da Iran ta harba zuwa cikin ƙasar, kuma tana ƙoƙarin kakkaɓe su domin kare rayuka da dukiyoyi.
A gefe guda, Qatar ta bayyana cewa an kai hari kan wasu sansanonin sojin Amurka da ke ƙasarta, sai dai ta jaddada cewa an samu nasarar dakile hare-haren.
Haka kuma, Bahrain ta tabbatar da cewa an kai hari kan sansanonin sojin ruwan Amurka da ke ƙasarta, duk da cewa ba ta bayyana wace ƙasa ce ta kai harin ba.
Lamarin na nuna ƙarin tsananta rikicin tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya.
Iran Ta Kaddamar Da Hare-Haren Ramuwar Gayya Kan Isra’ila Da Amurka

