INEC Ta Yi Watsi Da Kiran A Sauke Shugabanta

Hukumar zaɓen Najeriya (INEC) ta yi fatali da kiraye-kirayen da wasu ke yi na a sauke shugabanta, Farfesa Joash Amupitan, daga muƙaminsa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, hukumar ta bayyana irin waɗannan kiraye-kirayen a matsayin hari ga dokokin da suka kafa ta.

A ranar Alhamis ne jam’iyyar ADC mai hamayya, ɓangaren David Mark, ta buƙaci Mista Amupitan ya sauka daga kujerarsa, inda ta zarge shi da nuna ɓangaranci a aikinsa.

Wannan mataki ya biyo bayan matakin da INEC ta ɗauka na amincewa da sunayen shugabannin jam’iyyar na ɓangaren David Mark, bisa umarnin kotu kamar yadda hukumar ta bayyana.

Sai dai INEC ta ce irin waɗannan kiraye-kirayen ba su da tushe, tana mai jaddada cewa doka ce ke tanadar naɗin shugaban hukumar da kuma wa’adinsa.

“Dokar Najeriya ce ta samar da hukumar INEC. Kuma doka ce ta tanadfi naɗa shugabanninta kuma wa’adinsu,” in ji sanarwar.

“Shugaban INEC ba yana aiki ne ga kowace jam’iyya ko wata ƙungiya. Don haka duk wasu kiraye-kirayen cire shi daga wajen doka cin zarafi ne ga tsarin zaɓen ƙasa,” kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

More from this stream

Recomended