
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta sanar da ranakun da ta shirya za ta gudanar da zabukan gwamna a jihohin Ekiti da Osun a cikin watan Yuni da Agusta na shekarar 2026.
Kamar yadda jadawalin da hukumar ta fitar ya nuna za a gudanar da zaben gwamnan jihar Osun a ranar 20 ga watan Yuni a yayin da za ayi zaben gwamnan jihar Ekiti a ranar 8 GA watan Agusta.
Mahmoud Yakubu shugaban hukumar ta INEC shi ne ya sanar da ranakun zaben a ranar Juma’a lokacin da yake rantsar da sababbin kwamishinonin zabe 6 da aka nada.
Yakubu ya ce kamar yadda doka ta bukata inda ta bukaci hukumar da ta fitar da sanarwar yin manyan zabuka kwanakin da basu gaza 360 ba kafin zabukan.
Ya ce bisa bin doka hukumar ta amince da jadawali da kuma shirye-shiryen zabukan Ekiti da Osun.