Hukumar zaɓe ta Najeriya, INEC, ta fara tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin duba korafe-korafen da wasu ke yi kan jadawalin zaɓen 2027, wanda ke nuna cewa za a gudanar da zaɓen ne a lokacin azumin Ramadan.
Hukumar ta bai wa al’umma tabbacin cewa tana tsaye wajen ganin an yi la’akari da bukatun kowane ɓangare na al’umma wajen tsara ayyukanta.
INEC ta sanar cewa zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisar dokokin tarayya zai gudana a ranar 20 ga Fabrairu, 2027, yayin da zaɓen gwamnonin jihohi da ƴan majalisar dokokin jihohi zai kasance a ranar 6 ga Fabrairu, 2027.
Sai dai wasu ƴan Najeriya, musamman musulmai, sun nuna damuwa kan yadda jadawalin zai sa zaɓen ya faɗa cikin watan azumi, abin da ke haifar da tunanin yiwuwar matsaloli ga masu kada kuri’a.
INEC Ta Fara Tattaunawa Kan Korafin Jadawalin Zaɓen 2027

