[ad_1]
Toshon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya takali shugaban kasa, Muhammad Buhari kan maganar dake cewa shugaban kasar yana da lafiyar sake tsayawa takara a karo na biyu saboda ya yi tafiyar mita 800 ranar Sallah a Daura.
Batun lafiyar Buhari ya jawo ce-ce kuce da dama inda wasu dake adawa dashi su ke neman shugaban da kada ya yi takara a karo na biyu saboda rashin koshin lafiya.
A shekarar da ta gabata shugaban kasar ya shafe kusan kwanaki 150 a birnin London yana jiyar wata cuta da ba a bayyana ba.
Garba Shehu mai magana da yawun shugaban kasar ya nemi wadanda suke adawa da takarar Buhari a karo na biyu kan batun koshin lafiya da su nemi wani batun na daban domin tafiyar da yayi mai tsayi haka ya tabbatar da cewa batun lafiyarsa ba matsala bace.
Amma, Atiku Abubakar ya saka wani hoto a shafinsa na Twitter yana motsa jiki inda ya rubuta “Ina sassarfa fiye da mil daya tare da motsa jiki amma zai zamo mini banbarakwai idan nace yan Najeriya su zaɓe ni saboda haka.”
[ad_2]