Tsohon shugaban mulkin soja a Najeriya, Yakubu Gowon, ya musanta jita-jitar da ake yaÉ—awa a kafofin sadarwa cewa Allah ya amsa rasuwa.
Wani mataimakinsa Adeyeye Ajayi ne ya bayyana haka wa kafar yaɗa labaran ƙasar.
Gowon dai shi ne wanda ya mulki Najeriya daga shekarar 1966 zuwa 1975 wanda a ƙarƙashinsa ne aka yi yaƙin Biafra (watau yaƙin basasa).