Ina Mamakin Yadda Rayuwa Tayi Juyin Waina Dani – Zainab Indomie

[ad_1]








Shahararriyar jarumar da tauraronta ya daina haskawa a Kannywood, Zainab Abdullahi wacce aka fi sani da Zainab Indomie ta bayyana cewa ba ta san yadda aka yi rayuwar jarumtarta ta susuce ba duk da daukakar da ta samu a masana’antar fina-finan Hausa a baya.

Jarumar ta ce ta samu daukaka tun tana karama, amma saboda kaddara ba ta san abin da ya faru ba yanzu ta rasa komai.

Zainab ta nemi yafiyar Allah akan jarabtar da take fuskanta, inda tace idan laifi ta aikata toh rabbi yayi mata rangwame, sannan kuma tace idan har da hannun wani a cikin lamarinta toh tana rokon Allah ya yafe masa.

Daga karshe ta roki Allah ya sanya ta da sauran jama’a a kan hanya madaidaiciya.




[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...