Hukumar Zaben Nigeria, INEC, Na Bukatar Naira Biliyan 189

[ad_1]

Shugaban hukumar zabe ko INEC, Farfesa Mahmud Yakubu ya jagoranci jami’ansa a gaban kwamitocin kula da harkar zabe na majalisar dattawan dana wakilai domin yin bayani dangane da kudin da suke nema na gudanar da zaben shekarar 2019.

Farfesa Mahmud Yakubu yace suna bukatar kudi kimanin Naira biliyan 189 ne da za su kasa gida hudu. A ciki za’a biya ma’aikata zabe da kwamgilar buga takardun zabe da bangaren gudanar da ayyukan zabe, sai kuma kudin da za’a ware domin bukatu na musamman.

Kwamitocin kasafin kudi na majalisun Nigeria sun gana da jami'an INEC

Kwamitocin kasafin kudi na majalisun Nigeria sun gana da jami’an INEC

Shugaban hukumar zaben y ace idan an yi la’akari da zaben shekarar 2015, Naira biliyan 120 ne kawai aka kashe. Amma yanzu hukumar na neman Naira biliyan 189, an samu karin Naira biliyan 69. Yace dalilin banbancin shi ne karin masu jefa kuri’a da aka samu. A shekarar 2015 mutane miliyan 70 ne aka yiwa rajista. Amma a wannan shekarar an samu karin mutane miliyan 12 da ‘yan kai. Idan aka kwatanta da na shekarar 2015 an samu mutane miliyan 82 da za su kada kuri’a a zaben 2019.

Sanata Suleiman Nazir shugaban kwamitin harkar zabe na majalisar dattawa yace zaman kwamiti daban yake. Idan sun gama abun da su keyi sai su kai gaban majalisun, ayi muhawara a kai.

Dangane da naurar nan mai tantance masu zabe, da ake cewa card reader da turance, Sanata Suleiman Nazir y ace naurar ce ta basu nasara a zaben 2015, saboda haka suka yi doka cewa ba za’a yi zabe a kasar ba sai da naurar. Naurar ta na hana yin magudi.

A saurari rahoton Medina Dauda

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...