Hukumar Hisbah ta kama mabarata 643 a Kano – AREWA News

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu mutane 643 da aka samu da yin barace-barace a wasu tituna na birnin jihar.

Ana zargin su ne da karya dokar jihar da aka kafa a watan Fabrairu da ta hana yin bara a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar,Lawan Ibrahim ya ce an kama mutanen ne a yankin Bata,titin Murtala Muhammad, Asibitin Nasarawa, Tashar jirgin kasa da kuma gaban Yahuza suya.

Yace wadanda aka kama sun haɗa da mata 416 da kuma maza 232.

Ibrahim ya ce hukumar zata cigaba da kama marabata da suke cigaba da karya dokar.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...