Hukumar DSS Ta Miƙa Walida, Wacce Wani Jami’insu Ya Dace, Ga Gwamnatin Jigawa

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya karɓo Walida Abdulhadi Ibrahim daga hannun Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), bayan kiranye-kirayen da jama’a suka dinga yi kan lamarinta.

Rahotanni sun nuna cewa Walida ta ɓace daga gidansu, inda daga baya iyayenta suka zargi wani jami’in DSS da sace ta. Ana kuma zargin jami’in da aurenta, inda ta haifi yaro a hannunsa tare da tilasta mata sauya addininta daga Musulunci zuwa Kiristanci.

Bayan ƙorafin da iyayenta suka shigar, an tsare yarinyar a hannun DSS na wasu kwanaki kafin a miƙa ta ga gwamnan.

Da yake karɓarta, Gwamna Namadi ya ce za a miƙa duk zarge-zargen gaban kotu domin a bi su ta hanyar doka, tare da tabbatar da cewa an yi wa kowa adalci.

Ya kuma jaddada cewa Walida ’yar asalin Jigawa ce, kuma gwamnatin jihar za ta kula da lafiyarta da tsaronta tare da taimaka mata ta murmure daga halin da ta fuskanta.

A cewar Aminiya, gwamnan ya karɓo ta ne a hedikwatar DSS da ke Abuja, tare da rakiyar wasu manyan jami’an gwamnati ciki har da kakakin majalisar dokoki, babban lauyan jihar da kwamishiniyar harkokin mata.

More from this stream

Recomended