Hatsarin Mota Ya Hallaka ’Yan Jarida 7 A Gombe

Akalla ’yan jarida bakwai ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu hudu suka jikkata sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da motar Kungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) a Jihar Gombe.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Litinin yayin da ’yan jaridan ke dawowa daga wani biki a yankin Gombe ta Kudu. Sun kasance cikin tawagar da ta je taya wani abokin aikinsu, ma’aikacin Gidan Talabijin na Kasa (NTA), murnar aure.

Shugaban Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) a Jihar Gombe, Samson Kaura, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce mutum 11 ne ke cikin motar. “Bakwai sun mutu a wurin, yayin da hudu suka samu raunuka daban-daban,” in ji shi.

Ya kara da cewa binciken farko ya nuna hatsarin ya faru ne sakamakon fashewar taya, kuma motar ba ta yi karo da wata mota ba.

More from this stream

Recomended