Ma’aikatar Lafiya ta ƙasar Lebanon ta bayyana cewa hare-haren Isra’ila sun kashe aƙalla mutum 300 tun bayan fara rikici da ƙungiyar Hezbollah a ranar Litinin.
Hukumar ta ƙara da cewa sama da mutum 1,000 sun jikkata sakamakon hare-haren da aka kai a wurare daban-daban na ƙasar.
A yankin gabashin Lebanon kuwa, rahotanni sun ce an kashe mutum 40 tare da jikkata wasu 41. Rundunar sojin Isra’ila (IDF) ta ce tana gudanar da wani aiki a yankin domin gano gawar wani matukin jirgin sama nata da ya daɗe yana ɓacewa, mai suna Ron Arad.
A wani ɓangare kuma, Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya yi gargaɗi ga shugaban Lebanon, Joseph Aoun. Ya ce ƙasar Lebanon za ta “ɗanɗana kuɗarta” idan gwamnatin ba ta iya ƙwace makaman ƙungiyar Hezbollah ba.
Hare-Haren Isrq’ila Sun Kqshe Aƙalla Mutum 300 A Lebanon

