Gwamnonin PDP sun gudanar da taro a jihar Delta

Gwamnoni da aka zaba ƙarƙashin jam’iyar PDP sun tattaru a Asaba babban birnin jihar Delta domin su tattauna batutuwan dake damun jam’iyar.

Gwamnonin da suka yi shigar gargajiya irin ta mutanen yankin kudu maso kudu sun gudanar da taron a gidan gwamnatin jihar dake Asaba a ranar Juma’a.

Sun samu tarba daga gwamnan jihar, Sheriff Oborevwori.

Taron na gwamnonin na zuwa ne dai-dai lokacin da jam’iyar ta PDP ke tsaka da fama da rikicin shugabanci da yaƙi ci yaƙi cinyewa.

More from this stream

Recomended