Gwamnonin Kudu Sun Jajanta Wa Kano Kan Gobarar Kasuwar Singa


Kungiyar Gwamnonin Kudancin Najeriya ta mika sakon ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Kano sakamakon gobarar da ta auku a Kasuwar Singa, wadda ta jawo asarar dukiyoyi masu yawa.

Shugaban kungiyar kuma Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun, ya bayyana alhininsa kan ibtila’in, yana mai cewa gobarar na daga cikin manyan masifun da suka taba faruwa a kasuwar. Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta lalata kadarori da kudinsu ya wuce naira biliyan biyar, ta kuma shafi fiye da ’yan kasuwa 1,000, yayin da mutum bakwai har yanzu ba a gano su ba.

A sanarwar da ya fitar, gwamnan ya tausaya wa ’yan kasuwar da suka yi asarar kayayyaki da muhallansu na kasuwanci, yana mai ba su kwarin gwiwar kada su karaya. Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin Kano za ta dauki matakan da suka dace domin tallafawa wadanda lamarin ya rutsa da su.

Haka kuma ya shawarci mahukuntan kasuwa da jami’an kananan hukumomi da su inganta hanyoyin kariya domin kauce wa sake aukuwar irin wannan gobara a gaba.

More from this stream

Recomended