Gwamnonin arewa maso yamma za su haɗa kai wajen bunƙasa noma da magance matsalar tsaro

Gwamnonin yankin arewa maso yamma sun amince su yi aiki tare wajen magance matsalar tsaro da kuma bunƙasa aikin gona a yankin.

Gwamnonin sun dauki wannan matsaya ne biyo bayan wani taro da suka yi ranar Talata a gidan gwamnatin jihar Katsina.

Taron ya samu halartar gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, Dauda Lawal Dare na jihar Zamfara, Ahmed Aliyu gwamnan jihar Sokoto, gwamnan Kebbi, Nasir Idris da kuma mataimakin gwamnan jihar Jigawa Aminu Usman sai kuma mai masaukin baƙi gwamnan jihar Katsina, Dr. Dikko Umar Radda.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ya bayyana cewa gwamnonin sun faɗi cewa yin aiki tare shi ne zai amfani yankin.

Ya ce dukkanin gwamnonin sun amince su yi aiki tare wajen inganta fannin noma ta hanyar samar da kayan aiki da kuma kasuwannin hada-hadar kayan abinci.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]