
Tsohon shugaban ƙasa, Muhammad Buhari ya karbi bakuncin tawagar wakilan gwamnonin jam’iyar APC a gidansa dake Kaduna a ranar Litinin.
Tawagar ta samu jagorancin, Hope Uzodinma gwamnan jihar Imo wanda shi ne shugaban gwamnonin jam’iyar APC ya ce sun kai ziyarar ne domin miƙa gaisuwar Sallah da kuma taya tsohon shugaban kasar murnar kammala azumin watan Ramadan.
A cikin gwamnonin da suka kai ziyarar akwai Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe, Uba Sani na Kaduna, AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, Abdullahi Sule na Nasarawa, Francis Nwifuru na Ebonyi, Nasir Idris na Kebbi, da kuma Lucky Aiyedatiwa na jihar Ondo.
Sauran gwamnonin da suka kai ziyarar sun haɗa da Monday Okpebholo na Edo, Usman Ododo na Kogi, Biodun Oyebanji na Ekiti, da kuma Hyacinth Alia na Benue State.