Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya umarci jami’an tsaro da su dauki tsattsauran mataki kan mutanen da suke aikin haÆ™ar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.
A wata sanarwa ranar Asabar, mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Idris ya ce tsawon shekaru hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na ruruta wutar rikicin yan bindiga da kuma sauran ayyukan laifi a jihar.
A cewar mai magana da yawun gwamnan ya ce lokaci ya yi da za a kawo karshen ayyukan haÆ™ar ma’adanan tare da aiwatar da matakan da za su kare lafiyar al’umma.
A saboda haka aka umarci jami’an tsaro da su yi ta maza su harbe duk wanda aka samu da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.
“Umarnin ya zama dole domin kare lafiya da tsaron al’ummar jihar Zamfara da kuma razana wadanda suke shirin aikata aiki irin haka.” a cewar sanarwar.