Gwamnatin Tinubu ta gaza magance ko matsala daya a shekara 2 – Bugaje

Usman Bugaje tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya ya ce gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ta kasa magance ko daya daga matsalolin da ta gada.

Bugaje ya bayyana haka ne lokacin da yake magana a cikin shirin Daily Politics na gidan talabijin din Trust TV a ranar Juma’a.

Ya ce gwamnatin Tinubu ta fi fifita siyasa akan gudanar da mulki a lokacin

“Akwai korafe-korafe ba a arewa kadai ba har da Lagos cibiyar shugaban kasar,” ya ce

Bugaje ya yi tambayar ko gwamnatin Tinubu ta cika alkawuran da ta dauka a lokacin yakin neman zaben 2023.

Ya ce har yanzu gwamnatin ta gaza magance wasu manyan matsalolin kasa da suka hada da talauci, matsalar tsaro  da bunkasa rayuwar al’umma wanda a cewarsa su ne kashin bayan cigaban kasa.

Ya kara da cewa maimakon haka anfi mayar da hankali kan kafa allunan yakin neman zabe ya cigaba da cewa wannan ce shekara ta biyu ta gwamnatin amma da wuya ka nuna wani abu da ta cimma.

More from this stream

Recomended