Gwamnatin tarayya ta sanar da ware Naira biliyan 5 ga kowace jiha ta tarayya, ciki har da babban birnin tarayya domin rage tasirin cire tallafin man fetur.
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Alhamis lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a karshen taron majalisar tattalin arzikin kasa.
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya jagoranci taron.
Majalisar dai ta kunshi gwamnonin jihohi 36, da gwamnan babban bankin Najeriya da sauran jami’an gwamnati.