Gwamnatin tarayya ta yi tayin biyan ₦62,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Biyo bayan shafe sa’o’i da dama ana ganawa ranar Juma’a gwamnatin tarayya da kuma ɓangaren kamfanoni masu zaman kansu sun ƙara tayin da suka yi na mafi ƙarancin albashi daga ₦60,000 zuwa ₦62,000.

Amma kuma gamayyar kungiyoyin ƙwadago sun miƙa tayin ₦250,000 ragi daga ₦494,000 da suka bukaci a riƙa biya a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Hakan ne ya kawo ƙarshen taron ganawar da kwamitin ɓangarori da uku da gwamnatin tarayya ta kafa bayan watanni da dama.

Za miƙa matsayar da aka cimma ga shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu wanda ake sa ran zai tura kuɗirin dokar sabon ƙarin albashin ga majalisar ƙasa.

A wani ɓangaren gwamnonin Najeriya ƙarƙashin ƙungiyar su sun fitar da wata sanarwa dake cewa baza su iya ₦60,000 ba a matsayin mafi ƙarancin albashi.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...