Gwamnatin tarayya ta yi tayin biyan ₦62,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Biyo bayan shafe sa’o’i da dama ana ganawa ranar Juma’a gwamnatin tarayya da kuma ɓangaren kamfanoni masu zaman kansu sun ƙara tayin da suka yi na mafi ƙarancin albashi daga ₦60,000 zuwa ₦62,000.

Amma kuma gamayyar kungiyoyin ƙwadago sun miƙa tayin ₦250,000 ragi daga ₦494,000 da suka bukaci a riƙa biya a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Hakan ne ya kawo ƙarshen taron ganawar da kwamitin ɓangarori da uku da gwamnatin tarayya ta kafa bayan watanni da dama.

Za miƙa matsayar da aka cimma ga shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu wanda ake sa ran zai tura kuɗirin dokar sabon ƙarin albashin ga majalisar ƙasa.

A wani ɓangaren gwamnonin Najeriya ƙarƙashin ƙungiyar su sun fitar da wata sanarwa dake cewa baza su iya ₦60,000 ba a matsayin mafi ƙarancin albashi.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...