Gwamnatin tarayya ta hana sayar da iskar gas ƙasashen waje

Gwamnatin tarayya ta sanar da hana sayar man iskar gas na LPG da ake girki da shi ya zuwa ƙasashen waje.

Ekperikpe Ekpo ƙaramin ministan harkokin mai ɓangaren iskar gas shi ne ya sanar da haka ranar Alhamis a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki.

Ya ce matakin an ɗauke shi ne da gangan domin tabbatar da wadatuwar iskar a kasuwar cikin gida da kuma sauƙaƙawa mutane saboda yadda gas ɗin yayi tsada.

Ya ƙara da cewa tabbas idan aka samu wadatuwar iskar gas ɗin to kuwa babu makawa farashinsa zai yi ƙasa.

” Ina magana da hukumar NMDPRA dake saka ido muna yin taruka kusan kullum da kuma kamfanonin da suke samar da gas irinsu Shell,Mobil da Cheveron akwai fatan cewa abubuwa za su canza. Bama buƙatar muyi ta surutu akan batun.” Ya ce

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...