Gwamnatin Tarayya Ta Bawa Al’ummar Mokwa Tallafin Naira Biliyan Biyu

Mataimakin shugaban kasa,Kashim Shettima ya sanar da cewa gwamnatin tarayya ta bayar da tallafin naira biliyan biyu ga al’ummar da ambaliyar ruwa ta yiwa mummunar barna a garin Mokwa hedkwatar karamar hukumar Mokwa ta jihar Neja.

Shettima ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido garin domin jajantawa al’ummar da abun ya shafa.

Ya kara da cewa gwamnatin tarayya tayi alkawarin samarwa da mutanen tallafin gaggawa.

” A yau  na ziyarci al’ummar da ambaliyar ruwa ta shafa inda gwamnatin tarayya ta bayar da tallafin naira biliyan 2 da kuma motoci 20 na hatsi ga mutanen da abun ya shafa,”a cewar Shettima cikin wani sako da ya wallafa a Facebook.

A yayin ziyarar Shettima na tare da ministan yada labarai, Mohammed Idris Malagi

More from this stream

Recomended