Gwamnatin Tarayya ta ƙara kuɗaɗen makarantun sakandarenta zuwa N100,000

Kwalejojin Gwamnatin Tarayya (FGCs), wanda aka fi sani da Federal Unity Colleges, yanzu suna karbar kudin karatu fiye da da, wanda daga 45,000 ya tashi zuwa 100,000.

An bayyana hakan ne a cikin wani umarni da aka aika zuwa ga dukkan shugabannin Kwalejin Unity ta Tarayya a ranar 25 ga Mayu, 2023, mai lamba ADF/120/DSSE/I, daga ofishin daraktan Sashen Ilimi na Babbar Sakandare na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya.

Takardar da Daraktar manyan makarantun gaba da sakandire Hajiya Binta Abdulkadir ta sanya wa hannu ta bayyana cewa ana sa ran sabbin dalibai za su fara biyan ₦100,000 maimakon ₦45,000.

Hakan dai na zuwa ne duk da cewa majalisar wakilai ta bukaci gwamnatin tarayya a ranar 11 ga watan Yuli da ta daina kara kudin karatu a dukkan makarantun sakandare mallakar gwamnatin tarayya.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...