Gwamnatin ta tarayya ta ayyana ranar Laraba a matsayin hutu.

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutu domin bikin ranar dimakwaradiya.

Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ya ayyana haka a madadin gwamnatin tarayya a ranar Talata cikin wata sanarwa da Dr Aishatu Gogu Ndeyako babbar sakatariya a ma’aikatar cikin gida ta fitar.

Tunji-Ojo ya yadda cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu na cigaba da mayar da hankali wajen kawo kyawawan sauye-sauye da za su farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa.

” A yayin da muke bikin ranar dimakwaradiya a tarihin  Æ™asar mu.Ya kamata muyi duba kan Æ™oÆ™arin da waÉ—anda suka samar da Æ™asar suka yi ta hanyar tabbatar da Najeriya ta cigaba da zama dunÆ™ulalliyar Æ™asa mai cike da tsaro da zaman lafiya,” ya ce.

Ya kuma ya yi kira gan Æ´an Najeriya dama kawayen Najeriya da suyi duba su yaba cigaban da aka samu.

More from this stream

Recomended