Gwamnatin Najeriya za ta biya alawus ɗin N-Power na wata tara

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na fara biyan bashin watanni tara ga masu cin gajiyar shirin N-Power da ke shirin farawa daga watan Nuwamba.

Ta bayyana hakan ne a ranar Litinin ta bakin Manajan shirye-shiryen N-Power na kasa, Akindele Egbuwalo, wanda ya bayyana hakan a wata ganawa da wasu masu cin gajiyar N-Power a ofishinsa da ke Abuja.

Egbuwalo a wata sanarwa da ma’aikatar kula da jin kai da yaki da fatara ta tarayya ta fitar, ya bayyana cewa babbar manufar dakatar da shirin na wucin gadi shi ne a magance duk wani abu da ya shafi masu cin gajiyar shirin kai tsaye.

A cikin sanarwar ya bayyana cewa, sakamakon dakatar da shirin na wucin gadi da aka yi na yin gyaran fuska da kuma binciken kwakwaf, an kwato kudade daga hannun wasu a ciki.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...